Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Advertise on podcast: Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare

Categories
This podcast has
25 episodes
Language
Publisher
Explicit
No
Date created
2015/07/07
Latest episode
2026/04/23
Average duration
11 min.
Release period
8 days

Description

Shiri ne na musamman, da kan tattaunawa da bangarori daban-daban na Al’umma da ke sauraren Shirye shiryen RFI Hausa daga kowane kusurwa na fadin duniya, kan muhimman batutuwa, da suka shafi siyasa Tattalin’ariziki, al’adu da dai sauransu…

Unlock Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare podcast Email contact info,
Listeners & Audience details

Email contact information

Direct podcast contact details

Listeners

Audience numbers & engagement insights

Audience details

Podcast Insights

Social media

Check Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare social media presence


Podcast episodes

Check latest episodes from Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare podcast


An fara shari'ar mutanen da ake zargi da yunkurin kifar da gwamnatin Tinubu
2026/04/23
A ranar Laraba ne aka fara shari’ar wasu mutane da ake zargi da hannu a wani yunƙurin kifar da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu gaban wata babbar kotu da ke Abuja. Gwamnatin Najeriya ta shigar da tuhume-tuhume guda 13 kan mutane shida, waɗanda suka haɗa da Janar mai ritaya, wani Kaftin ɗin sojan ruwa mai ritaya, da kuma wani sufeton ɗansanda. Karon farko kenan da aka ga shari’ar zargin yunkurin juyin mulki a kotun farar hula, sabanin yadda aka saba gani a bariki ko kuma kotun soji. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin.
more
Ra'ayoyin masu sauraro kan batutuwa mabambanta
2026/04/17
Yau  juma'a, rana ce da sashen Hausa na RFI ke bai wa masu sauraro damar bayyana ra'ayoyinsu kan batutuwan da ke ci musu tuwo a ƙwarya, kama daga tattalin arziƙin, siyasa, zamantakewa da dai sauransu. Latsa alamar sauti don sauraren ra'ayoyi mabambanta...
more
Ra'ayoyin masu sauraro kan biyan bashin Triliyan 3 da Najeriya ta yiwa fannin lantarki
2026/04/07
Gwamnatin Najeriya ta sanar da ware sama da Naira tiriliyan uku domin biyan bashin da ke wuyan ƙasar a ɓangaren wutar lantarki. Sanarwa daga fadar shugaba Bola Tinubu ta ce an ɗauki matakin ne bayan an yi bitar illahirin bashin da ke wuyan gwamnati tsakanin 2015-2025 wannan bashi biyan wannan bashi zai bayar da damar shawo kan mafi yawan matsalolin da ke haifar da ƙarancin wutar lantarki a Najeriya. Shin ko meye ra’ayoyinku a game da wannan mataki? Ko wataƙila hakan zai kai ga ƙara ingantar samar da wutar lantarki a Najeriya? Ku danna alamar sauraro domin jin cikakken shirin tare na Nasiru Sani
more
Ra'ayoyin masu saurare kan dokar samar da mataimakin shugaban ƙasa a Kamaru
2026/04/06
Majalisun dokokin Kamaru sun amince da dokar da ke bai wa shugaba Paul Biya damar ƙirƙiro muƙamin mataimakin shugaban ƙasa da ke iya maye gurbin shugaban idan buƙatar hakan ta taso. Wasu dai na kallon hakan a matsayin yunƙurin da Biya ke yi domin tsara wanda zai gaje shi, a daidai lokacin da ake gaba da ɗiga ayar tambaya dangane da yanayi lafiyar shugaban mai shekaru 93 a duniya. Ku danna alamar sauraro dimin jin cikakke shirin tare da Nasiru Sani.
more
Ra'ayoyin masu saurare kan yadda yaƙin Gabas ta tsakiya ya haddasa tsadar kayan masarufi
2026/03/23
An shiga mako na huɗu da barkewar rikicin Yankin Gabas ta Tsakiya, inda ɓangarorin da ke hannu a rikicin ke ci gaba da kai wa juna hare-hare tare da kashe mutane da kuma lalata cibiyoyin makamashi. Tuni dai hakan ya haifar da tashin goron zabi ga farshin abubuwa da dama sanadiyar hauhawar farashin mai a kasuwar duniya. Ku danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Kabiru Yusuf
more
Ra'ayoyin masu saurare kan matakin CAF na kwace nasarar AFCON daga Senegal
2026/03/19
Hukumar kwallon ƙafar Afrika ta sanar da ƙwace Kambun da Senegal ta lashe a gasar neman kofin nahiyar da aka kammala cikin watan Janairun da gabata tare da miƙa shi ga ƙasar Moroko. Wannan dai mataki ne da ya yi matuƙar girgizar masu shawar harkar ƙwallon ƙafa a sassan duniya, inda tuni Senegal a buƙaci a gudanar da bincike bisa zargin cewa akwai yiyuwar an bayar da rashawa ne don ƙwace wannan galaba. Ku danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Kabiru Yusuf.
more
Yadda farashin makamashi ya yi tashin gwauro zabi a duniya
2026/03/12
Yanzu haka farashin ɗanyen man fetur na ci gaba da hauhawa sakamakon yaƙin da Amurka da Isra’il suka ƙaddamar kan Iran, inda yanzu haka ake sayar da gangar mai fiye da dala 92 a kasuwar duniya. A wannan yanayi dai ko shakka babu, ƙasashe masu arzikin mai ne irinsu na Najeriya za su ci moriyar wannan rikici. Shiga alamar sauti, domin suararon cikakken shirin.
more
Yadda yaƙin Gabas ta Tsakiya ya haifar da tsadar makamashi a duniya
2026/03/04
A yayin da yaƙi tsakanin Isra’ila da Amurka da Iran ke daɗa rincaɓewa, an fara gani tasirinsa a kasuwar ɗanyen mai da makamashi ta duniya. Ko a Najeriya, ƙasar da ta fi arziƙin ɗanyen mai a Afirka, farashin litar fetur ya tashi, kuma masana sun ce ana iya ganin cigaba da tashin farashin makamashi. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin.
more
Ra'ayoyin masu sauraro kan harajin yin wa'azi da ƴan bindiga suka sanya a Kebbi
2026/02/23
A Najeriya wata ƙungiyar ta'addanci da ba’a kai ga tantace wa ba, ta buƙaci a’ummar Utono ta ƙaramar hukumar Ngaski a jihar Kebbi da ta biya su zunzurutun ƙudi har Naira miliyan 100, kafin su bai wa malamai damar gudanar da Tafsiri ko wa’azi a wannan watan Azumi na Ramadana. Ƴan ta'addar sun bayyana bukatar ne a wata rubutacciyar wasika da suka aika garin na Utono. Wannan dai shine karon farko da wata ƙungiya da bukaci malamai biyan wani kudi domin gabatar da wa’azi, ko da ya ke al’umma a wasu yankunan sun saba biyan kudi don neman yancin walwa, ko ayyukan noma ko ma girɓi. Yaya kuke kallon wannan sabon bukata na ƴan ta‘adda? Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
more
Ra'ayoyin masu sauraro kan fargabar fuskantar ƙarancin abinci saboda gobarar Singa
2026/02/19
Dai dai lokacin da al’ummar musulmi suka faro azumin watan ramadana, can a jihar kano ta arewacin Najeriya da sauran jihohi maƙwabtanta, jama’a ne suka shiga cikin fargabar yiwuwar fuskantar hauhawar farashin kayakin masarufi sakamakon mummunar ɓarnar da gobara ta yi a kasuwar singa da ya haddasa ƙarancin kayakin na masarufi a kasuwannin jihar, kasancewar kasuwar ta singa babbar kasuwar da ke samar da kayakin Masarufi a kusan dukkanin arewacin Najeriyar dama wasu ƙasashen maƙwabta. Ku danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Kabiru Muhammad Ɗan Bauchi.
more
Ra'ayoyin masu saurare kan zanga-zangar ɗalibai a jamhuriyar Nijar
2026/02/10
Ra'ayoyin masu saurare na wannan rana ya mayar da hankali ne kan yadda ake juyayin cika shekaru  36 da jami’an tsaro suka buɗe wuta kan ɗalibai da ke zanga-zangar neman kyautata ilimi, yin fatali da tsare-tsare Asusun Lamuni na Duniya da sauran matakai na tsuke bakin aljihun gwamnatia jamhuriyar Nijar, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar aƙalla ɗalibai uku. Ku danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Kabiru Yusuf.
more
Ra'ayoyin masu saurare kan matakin IPOB dakatar da zaman gida na tilas duk Litinin
2026/02/09
Ƙungiyar ƴan awaren IPOB, da ke fafutukar kafa ƙasar Biafra ta sanar da janye matakin tilastawa jama’a zaman gida a kowace litinin da aka shafe shekaru biyar ana yi a yankin kudu maso gabashin Najeriya. Ku danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Kabiru Yusuf don jin cikakken shirin.
more
Ra'ayoyin masu sauraro kan kyautar Grammy da Fela Kuti ya samu bayan rasuwarsa
2026/02/03
Shekaru 29 bayan mutuwarsa, an bai wa shahararren mawaƙi kuma mai fafutuka Fela Kuti ya kasance ba’Afirke na farko da aka bai wa kyautar yabo ta Grammy wato Lifetime Achievement Award da ake bai wa wanda ya sadaukar da rayuwarsa yana rera waƙa. Fela ɗan Najeriya, ya yi fice ainun, ta hanyar rera waƙoƙin gwagwarmaya da kuma muradun talakawa. Shin ko me za ku iya tunawa a game Fela Kuti? Me za ku ce a game da wannan kyauta ta Grammy Awarda aka bayar bayan rasuwarsa? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Latsa alamar sauti don sauraren shirin...
more
Ra'ayoyin masu sauraro kan batutuwa mabambanta
2026/01/16
Yau  juma'a, rana ce da sashen Hausa na RFI ke bai wa masu sauraro damar bayyana ra'ayoyinsu kan batutuwan da ke ci musu tuwo a ƙwarya, kama daga tattalin arziƙin, siyasa, zamantakewa da dai sauransu. Latsa alamar sauti don sauraren ra'ayoyi mabambanta...
more
Ra'ayoyin masu sauraro kan yadda wasan kusa da na ƙarshe ya gudana a AFCON
2026/01/15
Morocco da Senegal sun yi nasarar kaiwa wasan ƙarshe na gasar cin kofin Afrika ko kuma AFCON, nasarar da suka samu bayan ita mai masaukin baƙi ta doke Najeriya yayinda Senegal kuma ta doke Masar dukkaninsu a daren jiya Laraba, yayinda ake shirin haɗuwa don doka wasan ƙarshe na gasar tsakanin manyan ƙasashen 2 a ranar Lahadi.   Anya kuwa ƙasashen na Masar da Najeriya sun taka rawar da ta dace gabanin fitar da su daga gasar? Wacce ƙasa kuke ganin za ta kai tsakanin labari wajen lashe kofin a wannan karon? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku akai. Latsa alamar sauti don sauraren shirin....
more

Podcast reviews

Read Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare podcast reviews


0 out of 5
0 reviews

Podcast sponsorship advertising

Start advertising on Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare & sponsor relevant audience podcasts


What do you want to promote?

Ad Format

Campaign Budget

Business Details